A Bauchi: Hukumar lafiya ta jinjina wa shugaban karamar hukumar Misau

Tura wannan Sakon

Jamilu Barau Daga Bauchi

Hukumar lafiya ta jihar Bauchi ta yaba wa shugaban waramar hukumar Misau Alhaji Abubakar Ahmad (Garkuwan Misau).

Jawabin hakan ya fito daga bakin jami’in kiwon lafiya na karamar hukumar Misau Alhaji Jibrin Ibra­him Muhammed, yayin wata bita na karawa juna sani kan aikin riga kafin cutar shawara watau ‘Yel­low Feber’.

Ya ci gaba da cewa ya­bon ya biyo bayan hadin kai da goyon baya da shugaban yake ba su na yau da kul­lum domin ganin al’umma suna amfana da magungu­nan da hukuma suke koka­rin bayarwa na lafiya.

A Satin nan dai huku­mar lafiya ta kaddamar da riga kafin shawara,

Shugaban karamar hu­kumar ya tara kansilolinsa da zaurawa da masu un­guwanni domin wayar wa jama’a da kai dangane da wannan allura.

Shugaban karamar hu­kumar Misau Abubakar Ahmad Garkuwan Misau, ya bayyana godiyarsa da wannan karramawa, ya kuma yabawa shi kansa Galadiman magani na ka­ramar hukumar Misau bisa ga kokarinsa ne yasa har shi ma ya samu lambar yabo.

Ya yi kira ga al’umma da su fito domin yin rigaka­fin shawara ba ta da wata Illa, ya nuna godiyarsa ga al’umma bisa ga yadda suke fitowa lungu da sako domin yin rigakafin.

Daga karshe ya godewa gwamna tare da jagororinsa kamar yadda suke bayar da kulawa ga al’umma musam­mam ta fannin kiwon lafiya.

Da fatan Allah ya kara­wa gwamnatin mu albarka, ya ba su ikon sauke nauy­in da Allah ya dora masu, Amin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *