A Damaturu: Kwalejin Kimiyya ta tarayya ta dauki dalibai 1,546

Yajin ASUU: Mun yi iya bakin kokarinmu -Gwamnatin tarayya

Malam Adamu-Adamu

Tura wannan Sakon

Sani Gazas Chinade, Daga Damaturu

kwalejin kimiyya da Fasaha ta Gwamnatin Ta­rayya da ke Garin Dama­turu cikin Jihar Yobe ta yi bikin kaddamar da Sababbin Daliban­ta na wannan shekakarar karatu ta bana 2019/2020 wadanda za su samu horo kan karatun kara­mar Diploma da babbar Diploma OND/HND su kimanin 1, 546.

Da yake jawabi yayin kad­damar da sababbin daliban a sab­on babban dakin taro na kwalejin Shugaban kwalejin Dr. Usman M. Kallamu ya bayyana cewar, wan­nan kaddamarwa Na dalibai ne ma su karatun karamar Diploma ND da babbar Diploma HND na shekarar karatu ta 2019/2020 su kimanin1,265 masu karatun ND da kuma 281 da za su yi karatun babbar Diploma a dukkan banga­rorin sashi-sashi na kwalejin.

Shugaban kwalejin ya kuma taya sabbin daliban murnar sa­mun wannan dama ta shigowa kwalejin wadda hakan ya ba su nasarar kawo wa ga matsayin rantsar da su bayan da suka yi ri­jistar shigowa kwalejin.

A cewarsa, “wannan dama da Ku daliban kuka samu na sa­mun sahalewar shugowa wannan kwaleji don gudanar da karatun da zai kai Ku ga cigaba ta ban­garen samun takardar karo karatu don amfanuwa ga samun rayuwa mai inganci har ila yau zai kuma sa Ku gyara halayyar Ku ta yadda zaku tafiyar da rayuwar ku dai-dai da bukatuwar al’ummomin ku

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *