A Jihar Yobe: Kwalara ta halaka mutane 3

A Jihar Yobe: Kwalara ta halaka mutane 3

Kwalara ta halaka mutane 3

Tura wannan Sakon

Sani Gazas Chinade Daga Damaturu

Akalla mutane 3 suka rasa rayukansu yayin da wad­ansu mutane 2 ke kwance a gadon asibiti sakamakon barkewar cutar kwalara a karamar hukumar Jakusko ta jihar Yobe cikin makon da ya gabata.

Bayanin hakan ya fito ne ta bakin Babban Sakataren Hukumar Lafiya a Matakin Farko na jihar Yobe, Dokta Babagana Kundi a jawabinsa ga manema labarai a garin Dama­turu.

Babban sakataren ya tabbatar da cewa, jin labarin hakan ya sa hu­kumarsa ba ta yi kasa a gwiwa ba, suka gaggauta tura wata tawagar gaggawa ta kwararru a yankin do­min shawo kan cutar gudin kar ta bazu.

A cewarsa tunin an shawo kan lamarin, kuma “na yi magana da shugaban tsare-tsare na cibiyar lafi­ya, inda na umurce shi da ya fara feshin maganin kashe kwayoyin cututtuka a yankin nan take ba tare da jinkiri ba domin gudun ci gaba da yaduwar annobar ta mai Baushe (Kwalara).

A nasa jawabin dangane da barkewar cutar ta kwalara a kara­mar hukumarsa, shugaban karamar hukumar Jakusko, Alhaji Abdul­lahi Hassan Gwayo, jan hankalin jami’an kiwon lafiyar da su dau­ki matakan gaggawa domin kare yaduwar cutar a wannan yanki da ma dukkan sassan jihar baki daya kasancewar cuta ce matukar hada­rin gaske da kan iya yaduwa babu kakkautawa da zarar an yi sakacin daukar mataki.

Shugaban ya kuma shawarci al’ummar da ke yankin da su duk­ufa wajen daukar matakin tsabtace muhallinsu, musamman wajen tsabtace abin sha da abincinsu da sauran mu’amullarsu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *