A Kano: Hukumar kashe gobara ta shirya fadakar da al’umma

Tura wannan Sakon

Daga Wakilinmu

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano, a ka­rkashin jagorancin Alhaji Hassan Ahmad Mu­hammad, ta kammala shirye shiryen da suka kamata, wajen fadakarwa tare da wayar da kan al’ummar jihar, musam­man a wannan lokaci da ake ciki na hunturu da kuma iska, domin kaucewa aukuwar tashin gobara a gidaje da ka­suwanni da sauransu.

Bayanin haka ya fito ne daga bakin mai kula da shash­in ma’aikatar, Alhaji Jamilu Bashir (HFS) a wata takar­da da ya sakawa hannu aka rabawa manema labarai. Al­haji Jamilu Bashir, ya kara da cewa, duk shekara irin wan­nan lokacin a kan fadakar da al’ummar jihar.

Tashoshin dake kwaryar birnin Kano sha biyar suma za su kaddamar da na su shi­rin wayar da kan a tashoshin kashe gobara sha biyu. Tashar kashe gobara dake garin Bi­chi, ita za ta kula da yankin masarautar dake masautan ta haka tashar dake garin Gaya da sauran su .

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano za ta sanaya idanu sosai aduk inda za’a gunar da aikin fadakarwa domin dai ganin shirin ya zamu nasaran da ake bukata da yardarm Al­lah inji Jamilu Bashir [HFS] FAIRE Prevention Officer.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *