A Neja: Sarkin Daji ya tallafa wa mata dubu 3 -Da jarin dubu 50-50

Alhaji Abdulma­lik Sarkin Daji,

Tura wannan Sakon

Daga Danjuma Labiru Bolari, Gombe

Kw a m i s h i n a n ma’aikatar kananan hukumomi na ji­har Neja, Alhaji Abdulma­lik Sarkin Daji, ya tallafa wa mata fiye da dubu 3000 da jari na Naira dubu 50 kowacce cikin shekara 2 a matsayin jari domin sauka­ke musu kuncin rayuwa.

Amina Abdulhamid Mina, Jakadiyar Malikiya, kuma shugabar mata ta kungiyar Dangin Juna Afir­ka Initiatibe, ne ta bayyana haka a lokacin da take zanta­wa da wakilinmu a Gombe a lokacin wani taron manema labarai da ta kira kan irin ci gaban da sarkin Daji ya kawo wa mata a jihar.

Amina Abdulhamid, ta ce, a duk fadin jihar Neja babu wani dan siyasa ko matashi da ya ke da irin halinsa domin a cikin shek­aru 2 na zamansa kwamishi­nan kananan hukumomi ne ya bar tarihin da ba za’a manta da shi ba.

Ta ce, a matsayin ta na Jakadiyar Malikiya ta han­nun ta kawai ta rarraba wa mata kudi fiye da Naira

miliyan 3, domin su ja jari a yankin Mashegu da Maruga da Wushishi.

A cewarta bayan wad­annan yankunan, alherinsa ya karade kaf illahirin jihar Neja wanda haka ta sa ake masa lakabi da farin jakada.

Ta yi amfani da wan­nan damar ta kirayi jama’ar jihar Neja da su yi koyi da irin halin Abdulmalik Sar­kin Daji Fari mai farar an­iya.

Sannan ta kirayi matan da ake bai wa tallafin da cewa, su dinga ririta wa, domin abinda suka samu domin su dogara da kansu domin ana ba su ne domin su samu madogara a rayuwa. Daga karshe, ta roki gwamnan jihar Neja da ya ci gaba da budawa kwamishi­nan domin ya ci gaba da tallafa wa marasa galihu, domin ragewa gwamnati dawainiya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *