A Sham: Jaura ta halaka jariran ‘yan-gudun hijira

A Sham: Jaura ta halaka jariran ‘yan-gudun hijira

A Sham: Jaura ta halaka jariran ‘yan-gudun hijira

Tura wannan Sakon

 Jarirai biyu sun rasa rayu­kansu a sakamakon tsananin sanyi bayan saukar dusar kankara a kan tantunan ‘yan gu­dun hijira a arewacin Syria.

Wani jami’in Majalisar Dinkin Duniya (UN) ya fada wa kamfanin labarai na AFP cewa, jaririya mai kwana bakwai da kuma ‘yar wata biyu sun mutu a yankin Idlib.

Mutane akalla miliyan biyu da dubu 800 ne suke zaune a sansanin ‘yan gudun hijira a yankin da ‘yan tawaye ke da karfi, bayan sun bar gidajensu sakamakon yakin basarar kasar na shekaru 10.

Da yawa na zaune ne cikin tsofaffin tan­tuna ba tare da kayan sanyi ba ko kuma maka­mashin dumama jiki.

Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa, lamarin na kara kazancewa saboda ta­barbarewar tattalin arziki a Syria, inda far­ashin kayan abinci ya ninka cikin shekara daya, da kuma karancin kudin bayar da tallafi domin sayen kayan sanyi da sauran bukatu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *