A soke lefe da kayan daki, a gyara sadaki -Sakamakon taro

Tura wannan Sakon

Daga Hassan Falaki Kulkul

A makon jiya ne, jaridar Al­bishir ta yi tattaki, inda ta ziyarci taron wata-wata na wata kungiya ta masu dalilin aure, da take gudanar da taronta a ma­karantar Alhaji Sani Buhari Daura (Walin Daura) da ke unguwar ‘Yar Maishinkafi, karamar hukumar Gwale, cikin birnin Kano.

Taron ya sami halartar shuga­bannin riko na kungiyar, da sauran ‘ya’yan kungiyar na kananan huku­momin jihar Kano. A wajen taron, an gabatar da addu’o’i na musam­man, ga tsohon shugaban kungiyar, Alhaji Danbala Warure,inda jari­dar ta tattauna da wasu shugaban­nin mata, da suka hadar da; Hajiya Asabe Dandago, Hajiya Halima Rogo, da Hajiya Asma’u Dawakin­Tofa, da Hajiya Rabi’atu Lawan Ri­jiya Hudu, kan zamantakewar aure, da yadda za a shawo kan maganin sake-saken aure, musamman a ka­sar Hausa.

Hajiya Dandago ta bayyana cewa, lamarin sake-saken aure abubuwa da dama ne suke kawo shi, a yanzu wannan abu ya tabarbare, domin a yanzu zawarawa sun ninka sosai, saboda mun tsinci kanmu a hali na tabarbarewar arziki, wanda wannan abu ya shafi duniya, san­nan ga rashin juriya.

Ita kuma a nata jawabin, Hajiya Asma’u Dawakin Tofa, ta bayyana cewa, yawan mace-macen aure ya ninka, a sanadiyar tabarbarewar tattalin arzikin kasa, sannan mu a karkara rashin ilimin zamantakewa, da sanin rashin hakkin ma’aurata, miji bai san hakkin matarsa ba, ita ma ba ta san hakkin mijinta ba, musamman ga bangaren maza, hakki ya rataya a kansu na ciyarwa.

Haka nan, Hajiya Halima Rogo ta ce, maganin mace-macen aure shi ne, yin adalci tsakanin ma’aurata, da taimakekeniya a tsakanin ma’aurata.

A karshe, Hajiya Rabi’atu La­wan Rijiya Hudu, karamar hu­kumar Dala, ta shawarci iyaye da masu neman aure kan cewa, a soke lefe, kuma a sok kayan daki, nau­yin ya koma kan mijin da zai auri matar, sannan a gyara sadaki yadda ya kamata.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *