A Zamfara: Iyaye sun ce ‘ya’yansu sun fara manta karatu

Iyaye sun ce ‘ya’yansu sun fara manta karatu

Tura wannan Sakon

Iyayen yara a jihar Zam­fara, sun yi kira ga gwamnati da ta dubi yi wuwar bude makarantu do­min hana dalibai ci gaba da gararamba kan titi.

Makarantun firamare da na sakandare a jihar sun kasance a rufe kusan wata biyu, a wani bangare na tsaurara matakan yaki da ‘yan bindiga da suka bullo da salon satar dalibai a ma­karantu.

Tun a ranar 1 ga watan Satumbar 2021, ne gwam­na Bello Muhammad Ma­tawalle, ya sanar da rufe makarantu, kama daga fi­ramare har sakandare, ya Allah jeka ka dawo ko na kwana da ke fadin jihar.

Hakan ya biyo bayan zafafa kai hare hare a ma­karantun sakandare har ma da na gaba da su.

Matakin gwamnatin na daukar wannan mataki ya zo ne jim kadan bayan sace daruruwan daliban ma­karantar sakandare da ke Kaya a karamar hukumar Maradun.

Kuma harin ya zo ne kasa da mako guda bayan sako daliban kwalejin kimi­yyar noma da kiwo da ke Bakura.

Tuni dai wasu iyayen yara suka fara nuna fargaba kan yadda ba bu wani bay­ani da ke fitowa daga bakin hukumomin jihar kan batun bude makarantu, duk da sa­mun haske a yaki da ‘yan bindigar.

Wani mahaifin daya daga cikin daliban da ke karatu a jihar ta Zamfara ya shaida wa BBC cewa, ‘yar­su har ta fara manya karatu, kuma ganin haka a yanzu shi da mahaifiyar yarinyar ne ke koyawa ‘yar ta su karatu a gida.

Mutumin ya ce, yaka­mata gwamnati ta dubi wannan yanayi da dalibai a jihar ke ciki, domin in ban­da gararanba ba bu abin da wasu daliban ke yi.

Ita ma wata mata da BBC ta ji bakinta a kan rashin bude makarantu a ji­har ta Zamfara, ta ce yaka­mata gwamnatin jihar ta su ta kalli abin da gwamnatin jihar Kaduna ta yi wajen bude makarantu duk da sa­tar daliban da ake yi a jihar.

Matar ta ce,” Gwamnat­inmu ta dauki mataki irin Kaduna, a samar da tsaro a makarantu sannan sai a bude su don yara su ci gaba da karatu”.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *