A Zamfara: ‘Yanbindiga sun kashe mutane 15 a Dutsin Gari

A Zamfara: ‘Yanbindiga sun kashe mutane 15 a Dutsin Gari

‘Yan bindiga

Tura wannan Sakon

Shu’aibu Ibrahim daga Gusau

Duk da irin tashin hankalin da al’ummar kauyen Dutsin Gari ke ciki na dauke wadansu ma­sallatan Juma’a a kwanakin baya, sai ga wani sabon hari da suka sake tsintar kansu a ciki a wannan makon wanda har ya yi sanadiyar kashe mutane 15.

‘Yan bindigar sun sake shigowa garin Dutsin Gari da Rayau da ke ka­ramar hukumar Maru, kamar yadda wani shaidun gani da idanu ya bayyana wa manema labarai ta wayar tafi da gi­dan ka, Malam Ibro Mamman wanda ya ce ‘yan fashin da ke kan babura sun mamaye kauyen Dutsin Gari a daren jiya da niyyar yin garkuwa da wadansu mutane amma mazauna garin sun yi al­washin ba za su sake bari a dauki wani a garin ba suka fuskance su har suka fa­tattake su, mutanen kauyen sun gwabza da ‘yan fashin inda suka dauki tsawon awanni ana artabu.

Mamman ya ce lokacin da ‘yan fashin suka fahimci haka, ba za su iya yin nasara a cikin mummunan aikinsu ba, sai suka bude wuta inda suka kashe mutane 15, suka ji wa da dama rauni sannan suka koma wani kauye da ke kusa da ake kira Rayau “.

“A kauyen Rayau, ‘yan bindigar sun kuma fuskanci irin wannan kalub­alen daga mazauna kauyukan wadanda suke a shirye domin karbar labarinka abin da ya faru a kauyen Dutsin Gari’

“Mazauna kauyen sun fito da yawa sun yi artabu da ‘yan bindigar inda biyu daga cikin mutanen garin suka rasa ra­yukansu kuma ‘yan bindigar suka tafi ba tare da sun kame kowa ba”. In ji Mamman.

Malam Mamman ya ce, ‘yan fashin sun sake komawa kauyukan da sany­in safiyar yau domin sun gano cewa, mazauna kauyukan da yawa sun bar garin sun gudu zuwa garin Kanoma sa­boda tsoron abin da zai je ya dawo, a dawowar na su sun bankawa gidaje da yawa wuta sannan suka tafi da dabbo­bin jama’a.

Idan za ku iya tuna wa cewa, a wad­ansu watanni a baya ‘yan bindigar sun shiga garin inda suka yi awon gaba da masallata masu sallar Juma’a su 40 ciki har da Limamin kauyen Dutsin Gari lo­kacin da ake sallar Juma’a a wani lokaci a baya.

An yi kokarin yin magana da ka­kakin rundunar ‘yan sanda, SP Mo­hammed Shehu, amma bai dauki kiran wayar ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *