An yi wa gwannan Zamfara riga-kafin korona

An yi wa gwannan Zamfara riga-kafin korona

An yi wa gwannan Zamfara riga-kafin korona

Tura wannan Sakon

Daga Shu’aibu Ibrahim Gusau

A yau ne aka kaddamar da al­luran rigakafin korona wanda gwamnan jihar Zamfara, Al­haji Bello Muhammad ya karbi allu­ran rigakafin a matsayin wanda aka fara da shi, an kaddamar da allurar ne a fadar gwamnatin jihar dake Gusau.

Bayan kammala yi masa allu­rar Matawallen maradun ya bukaci duk dan jihar Zamfara da ya aminta a yi masa allurar ta rigakafi, ya ce, rigakafi ne ga annobar da ake fama da shi a wannan kasa ta mu.

Ya kuma ce, za’a ci gaba da wan­nan allura zuwa ma’aikatun gwam­nati , ya ce, duk wanda ya ke so za’a yi masa, ya ce, kyauta ake yi ba’a bi­yan ko sisi

Shi ma a ci gaba da gudanar da allurar, Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Zamfara Mista Abutu Yaro, a ranar Talata, shi ma ya karbi kashi na farko na maganin korona.

Muhammad Sa’idu na asibitin ‘yansanda na Gusau ne ya ba shug­aban ‘yan sanda rigakafin, bayan

kammala wa shugaban ‘yansanda sauran manyan jami’an ‘yan sanda a jihar sun karbi allurar rigakafin a hedkwatar‘ yan sandan da ke Gusau.

Kwamishinan ya bukaci jami’an ‘yan sanda a jihar da su bayar da kan­su domin yin rigakafin, ya ce “Ina so in yi amfani da wannan damar in yi kira ga dukkan jami’an‘ yan sanda a jihar da su ba mu hadin kai a wannan aikin.

Alurar rigakafin ba ta da ciwo, ba ta da illa kuma tana da kyau a cikin jiki, domin yana amfani ga lafi­yar dan’adam, “A matsayinmu na jami’an tsaro, sai muna da koshin lafiya, za mu iya bayar da gudum­mawa ga tsaron kasarmu.

“An umarci dukkan ‘yan sanda maza da mata a jihar da su yi rajista kuma su tabbatar sun yi rigakafin.”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *