APC ta yi tir da kai wa ‘yan social media hare -hare -A Zamfara

Daga Shu’aibu ibarahim Gusau
Shugaban jam’iyyar APC na jihar Zamfara a karkashin tsohon gwamna Abdulaziz Yari Abubakar da Alhaji Lawal M. Liman, ya yi Allah wadai da hare-haren da ‘yan bangar siyasa ke kai wa masu mu’amulla da kafafen sadarwa na zamani watau (social media) da ke jihar Zamfara.
Hakan yana kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban kwamitin yada labarai na kungiyar Ibrahim Muhammad Birnin-Magaji ya fitar a Gusau a mokon da ya gabata. M. Liman ya bayyana haka ne a lokacin da yake mayar da martani kan harin da wadansu ‘yan daba suka kai wa shugaban jam’iyyar APC (Social Media Forum) APC ta yi tir da kai wa ‘yan social media hare -hare iya samun ci gaba a kasuwancinsu ba sai suna da yawan jari ba.
Shi ma shugaban taron kuma shugaban karamar hukumar Jos ta arewa, Shehu Bala Usman, ya yi jawabin godiya ya ce”ba kowa ba ne zai sami aikin gwamnati, sun shirya shirin kuma an fara a mazabar Garba Daho, ya kara da cewa, kowace mazaba an ba su Naira milliyan 2 domin fara shirin.
Shugaban ya sha alwashin tallafa wa harkar ilmi da kawo karshen sara suka da masu kwacen waya a cikin garin Jos, a nasa jawabin wanda ya shirya taron da daukar nauyi koyar da sana’o’i, kansilan mazabar Garba Daho, Auwalu Baba Ladan ya ce,”sun koyawa mutane 270 sana’oi daban-daban domin dogaro da kai.
Ya kara da cewa, sun kashe kudi fiye da Naira milliyan 2 domin bayar da gundunmawar su kansilan an yaba masa sosai yadda ya bayar da irin tallafin wannan shirin domin kawar da zaman banza. Shi ma Sulaiman Yahaya Kwande ya turo wakili da tallafin Naira dubu 50.
Daya daga cikin daliban da suka amfana Nafisa Sani Ibrahim, wacce ta koyi kwalliya ta nuna godiyar ta ga wannan kansilan, akwai dalibai da dama da suka koyi yin cake car wash da turare da dinki d shampoo da girkegirke da sauransu kuma sun ce ba su biya ko sisi ba, kansila shi ya dauki nauyin komai da komai. na bangaren Sanata Kabiru Garba Marafa da Malam Shamsu Kasida.
Ya kuma bayyana harin a matsayin wani salon adawar siyasa da bai dace da dimokradiyya ba, kuma babban abin damuwa ne ga duk ‘yan jihar masu son zaman lafiya da bin doka da oda. Ya kara da cewa“Bangaren Yari yana kara bayyana fargabar da take da shi a baya na cewa, jihar ta zama gidan wasan kwaikwayo na yakin siyasa, inda ‘yan daba ke mamaye fagen siyasa.
Ya ce“Harin, na daya daga cikin jerin shirye-shiryen, ya tabbatar da fargabar cewa, komai ba zai yi kyau a fagen siyasa nan gaba ba , idan har jami’an tsaro suka ki dakile shi tun yanzu. “Liman ya bayyana cewa, irin wadannan batutuwan idan har hukumomin da suka dace ba su amsa, yadda ya kamata ba yana iya rikidewa zuwa wani mummunan rikici da zai haifar da halaka ga al’umma mafi girma,” in ji shi.
Domin haka shugaban ya yi kira ga jami’an tsaro a jihar da su ci gaba da zama a sama wajen gudanar da aikin da ya rataya a wuyansu na tabbatar da zamani lafiya a Zamfara.
Ya jaddada cewa, babu wanda zai iya murkushe muryar ‘yan adawa a tsarin dimukradiyya ko ta yaya . Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Muhammad Shehu, ya ki cewa komai kan lamarin.