Bauchi ta dauki nauyin jiyyar Malama Asabe -Wadda aka nema wa taimako

Malama Asabe

Tura wannan Sakon

Jamilu Barau daga Bauchi

Gwamna Abdulkadir Mu­hammad ta dauki nauyin wata baiwar Allah datake fama da matsalar jinya Wanda ta­kici taki cinyewa gashi marasa karfine basuda komai ya kare a hannunsu.

Bayan gani da Kwamishinan Mata ta jihar Bauchi Hajiya Hajara Gidado a kafar sadarwa na yanar Gizo ba ta iya bacci ba cikin daren ta bayar da umarni lallai aka kira­ni na kira yan’uwan matan domin gwamanti ta taimaka masu.

Cikin ikon Allah ta yi tattaki tunda ga Bauchi ta je karamar Hu­kumar Katagum kauyen Tsuma­maro bisa yadda da amincewar Uwargidan gwamna Hajiya Aisha Bala Muhammad wadda a yanzu haka nan take kwamishiniyar mata ta jiha ta dauki Malama Asabe zuwa asibitin kwararru na jiha da ke Bauchi domin ba ta kulawa ta musamman kyauta.

Tabbas Hajiya Hajara Gidado dole mujinjina miki bisa gagaru­mar gudumawar da kika bayar na gaggawa domin kawo mata dauki karakashin amincewar uwar mara­yu, Hajiya Aisha Bala Muhammad Abdulkadir.

Tabbas kafa ta Social Media tana bayar da gudumawa matuka wajen isar da sakonni yadda ya ka­mata.

Muna kara Godiya wa al’ummah ma’abota kafa ta Social Media na irin gudumawa da kuka bayar, wajen yada wannan al’amari har akai ga mahukunta sun gani sun kuma dauki mataki.

Wadanda suka bayar da gudu­mawa ta kudi ta banki suma Allah ya saka masu da alheri an samu kudi ya kai kimanin 65,000 Allah ya bar zumunci yan’uwa da abokan gwagwarmaya Allah yakara dafawa wa gwamantin ji­har Bauchi, karkashin jagorancin gwamna Bala Muhammad Ab­dulkadir.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *