Bayan tashin-tashina, kura ta lafa a birni Jos -Gwamnati

Taro kan gyara kundin tsarin mulki: Lalong ya furta ra’ayinsa

Gwamna Lalong

Tura wannan Sakon

Gwamnatin jihar Filato, ta sanar da cewa, jami’an tsaro sun yi nasarar mayar da doka da oda a yankin Gada Biyu dake birnin Jos saka­makon tashin hankalin da aka samu ranar Litinin da ta gabata wanda ya haifar da kone-kone da kuma harbe-harben bindiga.

Wannan ya biyo bayan abin da ake dangantawa da yunkurin dau­

kar fansa da wadansu matasa suka yi sakamakon harin da aka kai karamar hukumar Bassa da ake zargin makiya­ya a kan ‘yan kabilar Irigwe abind a ya yi sanadiyar rasa rayuka da kuma kona gidaje.

Harin na zuwa ne kwana­kin bayan wani irinsa da aka kai karamar hukumar Riyom abin da ya sa majalisar tsaron jihar ta gudanar da taron gag­gawa, inda aka bai wa sojoji umurnin kara yawan jami’an su a yankunan kananan huku­momin da ake samun tashin hankalin.

Sanarwar da Daraktan yada labaran gwamnatin ji­har, Dokta Makut Simon Ma­cham ya rarraba wa manema labarai ta tabbatar da tura jami’an tsaron da kuma kwantar da tarzomar.

Macham ya ce, mata­kin ya biyo bayan harin da aka kai wa wadansu motoci guda biyu da kuma cinna masu wuta lokacin da matasa suka tare babbar hanyar Gada Biyu.

Gwamnatin jihar ta gar­gadi jama’ar jihar da su kauce wa daukar doka a han­nunsu wajen tare hanya suna kai hari a kan matafiya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *