Bunkasa ilimi: Shehu Bala Usman ya cancanci yabo – Jama’ar gari

Alhaji Shehu

Tura wannan Sakon

Daga Mohammed Ahmed Baba Jos

Alhaji Shehu Bala Usman shi ne shugaban kara­mar hukumar Jos ta are­wa, ana yaba masa da irin namijin kokarin da yake yi tun kafin ya hau kujerar Shehu Bala ya rike mat­sayin sakataran karamar hukumar Jos ta arewa, tun daga wannan lokacin.

Ya yi wa al’umma ayyukan ci gaba inda tun daga a wannan lokaci a shekarar 2016 ya samarwa mutane 13 gurbin karatu a jami ar Jos, kuma yake biya masu kudin makaran­ta a shekarar 2017 ya sa­marwa mutane 4 gurbin karatu Suma a jami ar ta jos, sannan akwai.

Mutane 70 da ya samar musu koyarwa a makaran­tar firamare sannan akwai mutanen da suka sami ai­kin ( cibic Defence) su 13 a shekarar 2016 mutane 4 sun sami aikin (Air force) da kuma mutane 5 da ya samarwa aiki a ma aikatar karamar hukuma, a fannin sana oin hannu an koyawa.

Marayu 35 sana’o’i da kuma tallafa masu a ban­garori da dama, domin sa­mun saukin rayuwa yawa­ncin wadannan ayyukan ya yi su ne lokacin yana matsayin sakataran ka­ramar hukuma, wannan ayyuka da ya yi ne yasa mutane da dama suke kira cewa, ya fito.

Takarar shugaban ka­ramar hukumar Jos ta are­wa, kuma bayan ya fito yayi nasara a zaben fitar da gwani a jam’iyyar Apc, sannan gwamna Simon Lalong ya tabbatar mai da kujerar ta shugaban kara­mar hukumar, inda nan gaba za a gudanar da zabe a watan oktoba.

Mai zuwa na kananan hukumomi inda a baya ba a gudanar da zabe a kananan hukumomi guda hudu ba, kamar Jos ta arewa Jos ta kudu, basa da Riyom saboda matsal­ar tsaro, amma a wannan karon gwamnati ta tab­batar da cewa za a yi za­ben gaba daya a kananan kumomin.

A fadin jihar Filato a watan 10 mai zuwa bayan ya zama shugaban kara­mar hukumar ya bayar da (transformer)a unguwan­nin mudi na garba, haruna hadeja, da kuma unguwar idi mai borkono, sai un­guwar rimi inda matasa kimanin 15 da suka sami aikin soja.

Da kuma mutanen da shugaban ya bai wa tallafin karatu a jami’ar Jos matai­maki na musamman akan ayyukan yau da kullum, ga shugaban Muhammad shala ya bayyanna cewa, an yi aikin ruwa inda aka saka fanfunan ruwa da ma­karantun firamare da suka sami tallafi.

Kamar makarantar is­lamiyya dake bauchi road wacce itace mafi dadewa a garin Jos da makarantar U.N.E. da ke Nasarawa, da sauransu ya ce” suna aiki Musulmai da Kirista tare a karkashin shugaban domin kara hadin kai da zaman lafiya a garin Jos, da ungu­wanni.

Shugaban ya tabbatar da tsaftar muhalli, na wata wata wanda a baya dokar ta yi sanyi an tabbatar da hana cinkoso a babbar kasuwar terminus da titin Ahmadu Bello inda a baya abin yake ci wa mutane tuwo a kwarya, amma yanzu jama’a suna yaba wa saboda doka.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *