D/Tofa ta sami yabo saboda gina hanyar Babbar Ruga-Fango

Tura wannan Sakon

Jabiru A Hassan Daga Kano

Al’umomin garuru­wan Babbar Ruga zuwa Fango sun yaba wa majalisar kka­ramar hukumar Dawakin Tofa bisa jagorancin Al­haji Ado Tambai Kwa sa­boda aikin hanyar su da ya ke yi wadda suka dade suna fatan ganin an samar da ita.

Wakilinmu wanda ya ziyarci garuruwan da hanyar ta ratsa, ya ru­waito cewa, aikin yana tafiya cikin nasara, san­nan akwai alamun cewa, kamfanin da ke gudanar da aikin zai kammala ta kan ka’idar da aka yi duk da cewa, yanzu ana cikin yanayi na damina.

Gaskiya Tafi Kwabo ta zanta da wadansu mu­tane yayin da wakilinmu ke duba yadda aikin han­yar ke tafiya, inda duk­kanin wadanda suka yi magana kan aikin hanyar suka bayyana jin dadinsu saboda ganin za’a samar da hanya mai kyau duba da yadda ake da garuruwa masu yawa masu amfani da hanyar.

Malam Adamu Chedi Babbar Ruga yace “ gas­kiya idan aka kammala hanyar mun sami damar rubanya harkokinmu na sufuri tare da fito da kay­an amfanin gonakinmu cikin nasara, domin haka muna godiya da shugaba Alhaji Ado Tambai Kwa bisa namijin kokarin da yake mana”. In ji shi.

A garin Fango, wakilinmu ya gana da Malam Jafaru direba wan­da ya bayyana jindadi dangane da aikin hanyar, tare da jaddada cewa, ma­jalisar karamar hukumar Dawakin Tofa ta yi masu komai duba da yadda ai­kin hanyar zai zamo alheri garesu, ya yi fatan cewa, al’ummar yankin za su ci gaba da bai wa karamar hukumar goyon baya da hadin kai.

A nasa bangaren, shugaba Ado Tambai Kwa ya shaida wa wakilinmu cewa, za su ci gaba da gu­danar da ayyukan, domin ganin kowace mazaba ta amfani ribar dimokuradi­yya tare da jaddada cewa, gwamnatinsa tana aiki ne bisa la’akari da bukatun al’ummar yankin, inda kuma ya gode wa gwamna Ganduje saboda kulawa ta musamman da yake bai wa kananan hukumomin jihar Kano.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *