Ganduje, ginshikin ilimi, tauraron gwamnoni -Garun-danga

Tura wannan Sakon

 Daga Salihu S. Gezawa

An bayyana gwamnan ji­har Kano, Dokta Abdul­lahi Umar Ganduje, a mat­sayin garkuwar ilimi kuma tauraron gwamnonin Arewa.

Sakataren ilimi na karamar huku­mar Gabasawa, jihar Kano, Malam Kabiru Yusuf Garun-danga shi ya yi batun, a lokacin da yake zantawa da manema labarai, inda ya ce, tabbas gwamna Abdullahi Umar Ganduje mikiya ne mai hangen nesa wanda ke da manufofi managarta da za su kai jihar Kano ga nasara.

Malam Kabiru Garun-danga ya ce, babu abin da jama’ar jihar Kano za su ce, sai godiya da sambarka do­min Gandujen kanawa ya fitar da kanawa kunya wajen ayyukan raya kasa, da inganta lafiya, raya karkara da kuma uwa-uba gina ilimi ta han­yar bai wa makarantun firamare ku­lawar gaske.

Garun-danga ya ce, hak­ika gwamna Ganduje gwar­zo ne abin koyi ta kowanne bangare tare da yin amfani da kwarewarsa wajen kawo ci gaban a zo a gani duk da yawan al’ummar jihar Kano.

Daga nan Garun-danga sai ya yi kira ga jama’ar jihar Kano da su ribanya goyon bayansu ga Khadimul Is­lam Ganduje wanda ya hana idonsa barci domin ganin ji­har Kano ta kara amsa suna­nta.

Da ya juya ga malaman firamare na karamar huku­mar Gabasawa, kira ya yi gare su da su kara himmawajen sauke nauyin da Al­lah ya dora masu na bayar da ilimi da tarbiyya inda ya ce, su sani amana ce da Allah ya ba su kuma zai tambaye su gobe kiyama.

Ya kuma yi kira ga iyayen yara na karamar hukumar da su rinka ziyartar makarantun yankin domin ganin irin yad­da harkar koyo da koyarwa ke tafiya. ya ce, harkar ilimi ta kowa ce, domin haka ya ce, akwai bukatar kowa ya shigo domin hada hannu da gwamnati wajen daga dara­jar ilimi a karamar hukumar da ma jihar Kano.

Daga nan ya gode wa shugaban karamar hukumar, Alhaji Mahe Garun-danga saboda goyon bayan da yake bai wa sashen ilimi na kara­mar hukumar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *