Kano ta rufe asibitin yara -Saboda rashin gamsuwa

Jihar Kano
Tura wannan Sakon

Daga Nasiru Muhammad

Gwamnatin jihar Kano da ke arewacin Ni­jeriya ta rufe ayyukan asibitin yara da ke titin Gidan Zoo a cikin birnin Kano bayan shafe kusan shekaru uku da fara aiki.

Matakin gwamnatin na Kano ya dai kawo tsaiko wajen harkokin duba marasa lafiya, sakamakon yadda ma’aikatan asibitin suka gaza sanin mako­marsu yayin da marasa lafiya ke kokawa.

Wakilinmu wanda ya zi­yarci asibitin yara na Isyaka Rabi’u da ke hanyar gidan ad­ana namun daji, ya ce a sabanin yadda asibitin ke cika makil da marasa lafiya da koke-koken yara, a yanzu shiru kake ji.

Wasu daga cikin marasa lafiya da ke jiyya da kuma ba a sallame su daga asibitin ba, sun yi tagumi suna tunanin a makomar rayuwa, sakamakon fargabar halin da za su shiga idan likitoci da malaman jinya suka daina zuwa aiki.

“Ba mu san makomar mu ba, saboda babu wani bayani da akai mana, wadanda ke kula da asibiti da shugabannin asi­bitin ne suka samu sabani, don haka sai an warware matsalar,” in ji shi. Sai dai shugaban hukumar da ke kula da asibitoci a Kano, Dr Nasiru Kabo, ya shaida wa BBC cewar gwamatin Kano ba ta rufe asibitin ba, amma ta janye yarjejeniyar kawance aiki tsakanin ta da kamfanin Northfield Health Services sa­boda rashin gamsuwa da yadda yake kula da asibitin

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *