Kasuwar ‘yan kwallo: Makomar Ronaldo, Kane, Benitez, Favre, Torres, Dumfries, Soumare, babu tabbas

Kasuwar ‘yan kwallo: Makomar Ronaldo

Cristiano Ron­aldo

Tura wannan Sakon

Shugaban Barcelona Juan Laporta na sha’awar hada Cristiano Ron­aldo da Lionel Messi su yi wasa a kungiyarsa a kakar wasa mai zuwa, kuma a shirye yake ya yi musayar dan wasansa biyu domin Juventus ta amince Ronaldo, dan wasan gaba, mai shekara 36, ya bar kungiyar. (AS – in Spanish)

Manchester City ta ce a shirye take ta mika dan wasan gaba kuma dan Bra­zil Gabriel Jesus, mai shekara 24, da Ra­heem Sterling, da wasan gaba na Ingila mai shekara 26 domin ta cima burinta na daukan Harry Kane daga Tottenham. An dai sa wa Kane farashin fam miliyan 150. (Times – subscription rekuired)

Manchester United na kan bakanta ta raba Pau Torres, dan wasan baya kuma dan kasar Spaniya mai shekara 24 da Vil­lareal. (Manchester Evening News)

Rafael Benitez na dab da zama sabon kocin Everton bayan ya sake tattaunawa da masu kungiyar a karshen makon jiya, duk da cewa magoya bayan kungiyar sun nuna rashin amincewarsu. (Mirror)

Crystal Palace kuwa tattaunawa ta yi da Lucien Favre domin y maye gurbin Roy Hodgson amma da alama Everton ma na son daukan shi. (Guardian)

Atalanta na fuskantar matsaloli wajen tsawaita kwantiragin Matteo Pes­sina, dan wasan tsakiya dan kasar Italiya, bayan da kungiyoyi biyu – AC Milan da Roma su ka bayyana cewa su na bukatar dan wasan mai shekara 24. (Calciomer­cato – in Italian)

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *