Makomar ‘yan gudun hijira: Nijeriya, Nijar za su yi mukabala

Makomar ‘yan gudun hijira: Nijeriya, Nijar za su yi mukabala
Tura wannan Sakon

Sabon shugaban Jam­huriyar Nijar Mo­hamed Bazoum, ya ce zai shiga tattaunawa da gwamnatin NIjeriya domin mayar da ‘yan gudun hiji­rar da suka tserewa matsalar tsaron da ake fama da ita a Najeriyar domin samun ma­faka a kasar ta Nijar.

Matakin dai na daga cikin alkawuran da sabon shuga­ban kasar na Nijar ya dauka a lokacin da yake gabatar da jawabi jim kadan bayan an rantsar da shi.

Yayin jawabin da ya ga­batar, Bazoum ya koka kan yadda ta’addanci ya zamewa Jamhuriyar Nijar babban bala’i duk da cewa sansanonin ‘yan ta’adda, da ma shugaban­ninsu na wajen kasar.

Yayin ranstuwar kama aiki a ranar 2 ga watan Afrilu, sabon shugaban Nijar Ba­ zoum Muhammad da ya zargi mayakan dake kai hare-haren ta’addanci a sassan kasar da aikata laifukan yaki.

Nijar na fama da hare-haren mayaka masu ikirarin jihadi dake biyayya da kungi­yar Al’kaida ko IS wadanda ke ketarawa cikin kasar ta bangaren yammaci daga Mali da Burkina Faso, sai kuma kungiyar Boko Haram da ke kaddamar da nata hare-haren bayan shiga kasar dta bangar­en kudu maso gabashi daga Nijeriya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *