Masu sace ‘yan-makaranta za su kashe ililmi a Arewa –Buhari

Tura wannan Sakon

Shugaban Nijeriya Muhammadu Bu­hari ya umarci so­joji da ‘yan sanda da sau­ran jami’an leken asiri da su tabbatar da an sako dukkan mutanen da aka yi garkuwa da su kuma cikin aminci.

Cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman kan kafafen yada labarai ga shugaban, Garba Shehu ya fitar ya ce, Buhari ya nuna damuwa game da ka­ruwar hare-hare a Kaduna da Neja musamman kan daliban makarantu.

Shugaban wanda ya ba da umarnin kara girke da­karun tsaro a yankunan da suke kara zama hadari, ya shawarci jami’an da su yi aiki da hankali da dabara wajen tabbaar da an sako daliban da aka sace cikin aminci.

Buhari ya ce, yawan sace daliban da ake yi a makarantu musamman a jihohin Arewacin Ni­jeriya zai haifar da wani gagagrumin koma baya ga harkokin ilimi, da kuma yadda iyaye za su rika kai yaransu makarantu.

Ya kuma yi kira ga gwamnatocin jihohi da su bayar da hadin kai ga shi­rin Majalisar Dinkin Duni­ya na tabbatar da aminci ga makarantu, wanda gwam­natin tarayya da runguma

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *