Mukabala: Kungiyar NACOMYO ta jinjina wa gwamnati

Mukabala: Kungiyar NACOMYO ta jinjina wa gwamnati

Mukabala

Tura wannan Sakon

 Daga Salisu Baso

An jinjina wa matakin gwamnatin jihar Kano, ka­rkashin jagorancin gwam­nan Kano, Dokta Abdullahi Umar Ganduje (Khadimul Islam) saboda bayar da damar tattaunawar ilmi tsakanin gamayyar Malamai da kuma Malam Abduljabbar Nasiru Kabara domin ba shi damar kare kansa kan kalaman da ya furta da suka danganaci martabar Manzon Allah SAW da sahabbansa masu daraja.

Shugaban majalisar kungi­yoyin matasan Musulmi ta kasa (NACOMYO) reshen jihar Kano, Malam Ahmad Abubakar Mai zube ya bayyana jin dadinsa a ga­nawarsa da manema labarai a ka­rshen taron kungiyar na yankin Arewa a jihar Kano, a makon da ya gabata.

Ya kuma gode wa kwamishi­nan ma’aikatar kula da harkokin Addinai, Dokta Muhammad TahirAdam Baba Impossible da shugabanni da ma’aikatan hukumar Shari’a ta jihar da kuma hukumomin tsaro saboda jajircewarsu wajen ganin an yi mukabalar cikin kwanciyar hankali da lumana.

Majalisar ta yi jan han­kali ga dukkanin matasa masu kokarin neman ilmi addini da su kasance masu kula da malaman da suke neman ilmi a gabansa do­min gudun fadawa cikin munana akidu masu riki­tarwa.

A karshe, majalisar ta yi kira ga gwamnatin jihar Kano da ta hanzarta daukar matakin da ya da ce a kan wanda ya furta munanan kalamai ga Manzon Al­lah (SAW) da sahabbansa domin zama darasi ga na

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *