Nan gaba kadan rikicin Boko-haram zai zama tarihi -Janar Attahiru

Babban hafsan sojin Nijeriya Janar Ibrahim Attahiru ya rasu

Marigayi Janar Attahiru

Tura wannan Sakon

Sani Gazas Chinade Daga Damaturu

Babban Hafsan Da­karun kasar nan, Manjo Janar Ibra­him Attahiru, ya bayyana cewa, nan ba da jima wa ba cikin ikon Allah riki­cin Boko Haram da ya dabaibaye wannan yanki na Arewa maso Gabas zai zama tarihi.

Babban Hafsan ya bayyana hakan ne a ziyarar da ya kai garin Ngamdu a jihar Borno, tare da cewa, za su hada kai da sojojin kasar Chadi domin kawo karshen mayakan Boko Haram ta ko halin kaka.

Janar din, ya jaddada hakan ne a yayin ganawar sa da manema labarai a garin Ngamdu, kafin nan sai da ya gana da jami’an sojojin da ke karkashin kulawarsa tare da yi masu alkawarin za a inganta aikinsu, da kuma samar masu kayan aiki domin magance wannan matsala ta ‘yan ta’adda; sai kuma ya tabbatar da cewa, za a share masu hawayensu a kan duk wadansu matsal­oli da ke addabarsu ba tare da bata lokaci ba.

Ya kara bayyana cewar shugaban kasa na nuna matukar damuwarsa da yadda ayyukan ta’addanci ke cigaba da habaka a wan­nan yankin, wadda hakan Na daga cikin masudin kawo wannan ziyara ta su da nufin karfafa musu gwi­wa a fafutukar da suke yi na kare rayukan al’umma da dukiyoyinsu da kuma diyaicin kasar nan.

A cewarsa sabbin tsare-tsare da suka fito da su ba wai don wani abu ba ne, illa su kawo karshen wan­nan yakin da ake gwabza­wa ne da wadannan ma su tada kayar baya na Boko Haram. Shine ma ya sa aka duba aikin rundunar sojin ta Tura Ta Kai Bango, za a ga cewar an samu nasarori da daman gaske matuka.

Don sum a halin yanzu suna son ne su dora daga inda aka tsaya akan yaki da ta’addanci da ake yi ta yadda sun daura damarar har sun ga bayansu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *