Neja ta rufe makarantun kwana bayan sace daliban Kagara

Neja ta rufe makarantun kwana bayan sace daliban Kagara
Tura wannan Sakon

Gwamnatin Jihar Niger dake Najeriya ta sanar da rufe dauka­cin makarantun kwanan dake kananan hukumomi 4 dake Jihar sakamakon sace daliban makaran­tar Sakandaren Kagara sama da 200 da Yan bindiga suka yi da asu­bahin yau.

Gwamna Abubakar Sani Bello ya bayyana Kananan hukumomin da umurnin ya shafa da suka hada da Munya, Mariga da kuma Shi­roro.

An bayyana sunan dalibin da Yan bindigar suka harbe har lahira lokacin da suka kai hari makaran­tar a matsayin Benjamin Doma.

Rahotanni sun ce Yan bindigar sun harbe Doma ne lokacin da yake kokarin tserewa daga makarantar, bayan anyi garkuwa da su.

Ya zuwa yanzu dai babu raho­tan dake nuna cewar Yan bindigar sun gabatar da bukatar su, yayin da shugaban kasa Muhammadu Bu­hari ya baiwa sojoji da Yan Sanda umurnin kubutar da daliban.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *