Rikici a Sudan ta Kudu: Fiye da mutane dubu sun salwanta

Tura wannan Sakon

 Kwamitin tsaro na maja­lisar Dinkin Duniya ta ce, fiye da mutane dubu suka rasa rayukansu cikin watan­ni shida, yayin da aka sace aqalla mutane 400 sakamakon rikice-ri­kicen qabilanci a Sudan ta Kudu.

Har yanzu Sudan ta Kudu na qoqarin murmurewa daga rikicin tsawon shekaru shida wanda ya ti­lasta wa gwamnati rarraba madafun iko a cikin watan Fabairu 2020, matakin da ya kawo qarshen tashin hankalin.

A baya-bayan nan dai, rikici ya tsananta tsakanin qabilu a qasar sakamakon dalilai mabambamta da suka hada da barnar da shanu ke yi wa manoma.

Babban Jami’in Ma­jalisar Dinkin Duniya na musamman a Sudan ta Kudu, Dabid Shearer ya ce, fiye da mutane dubu suka mutu a garin Warrap a cikin watanni shida kuma a yan­zu haka akwai mutane da dama da suka yi azamar qa­ddamar da hare-haren dau­kar fansa a cewarsa.

Jami’in ya yi gargadin cewa, rikicin qabilancin ka iya qazancewa da zarar an shiga lokacin rani nan da watan Janairu.

A can kuwa gabashin Jonglei, daruruwan mutane ne suka mutu a rikicin, san­nan fiye da mutane 400 aka

sace su, kuma akwai yiwu­war nan gaba kadan, tashin hankalin ya yi qamari a Jonglei a cewar Majalisar Dinkin Duniya.

Masu sanya ido sun yi gargadin cewa, rikicin qa­bilancin na yin barazana ga yarjejeniyar zaman lafiyar da aka cim ma a cikin watan Satumban shekarar 2018 domin kawo qarshen yaqin da ya laqume rayuka kusan dubu 400 a qasar.

mance, shekaru 40 da suka wuce.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Sin, Wang Wenbin ya fada a wani taron manema laba­rai cewa, lallai qasar na taya Joe Biden da Kamala Harris murnar lashe zaben.

Kafin yanzu, Sin na cikin wadansu manyan qasashen da ba su taya za­babben shugaban Amirka murna ba kamar su Rasha da Medico.

Tun da kafafen yada labran Amirka suka sanar da wanda ya samu quri’u mafi yawa a zaben shuga­ban Amirka, shugaba mai barin gado Donald Trump bai amince da shan kaye ba akasin yadda aka saba yi a qasar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *