Rundunar ‘yan-sanda ta bude sabon ofishin kwamanda na Shinkafi

Rundunar ‘yan-sanda ta bude sabon ofishin kwamanda na Shinkafi
Tura wannan Sakon

Daga Shu’aibu Ibrahim Gusau

Babban Sufeton ‘yan sanda (IGP), Muhammad Ad­amu, ya kaddamar da sa­bon ofishin kwamandan yanki a garin Shinkafi, a karamar hukumar Shinkafi da ke Zamfara.

Hakan ya fito ne daga jami’in hulda da jama’a na ‘yan-sanda na jihar, SP Muhammad Shehu, a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Gusau.

Ya kara da cewa, sab­on ofishin wanda Hedik­watar rundunar ’yan san­da ta gina kwamishinan‘ yansanda na jihar, Mista Abutu Yaro ne ya bude shi a madadin IGP.

Ya ce, aikin yana daga cikin kudurin da gwam­natin tarayya ke da shi na samar da kyakkyawan yanayin aiki ga jami’an ‘yan sanda don su sami damar sauke nauyin da ke kansu na kiyaye lafi­yar jama’a, domin samar da zaman lafiya, da tsaro a fadin kasar.

“IGP yayi kira ga jami’an ‘yansanda da mazaunan yankin su yi amfani da ofishin yad­da ya kamata da kuma abubuwan da aka samar a ciki.

Shehu ya ci gaba da yin kira ga al’ummomin yankin da ma sauran yankunan, da su nuna godiya ga wannan aikin ta hanyar tallafa wa ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro a kokarin da suke yi na shawo kan matsalolin tsaro da ke addabar jihar, “in ji Shehu.

Shugaban ‘yansan­da na jihar zamfara, CP Yaro, wanda tun da far­ko ya ziyarci sarakunan Zurmi da Shinkafi a wani bangare na ziyarar fahim­tar juna da ya yi wa sara­kunan gargajiya da masu ruwa da tsaki a harkar tsaro a jihar.

Ya gode wa masarau­tun biyu kan yadda suke aiki tare da ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro don tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin, ya ce “Ina neman karin goyon baya daga gare ku a wan­nan batun,” in ji CP .

A yayin ziyarar, ya yi jawabi ga jami’an ‘yansanda na rukunin Yankin Shinkafi da Zurmi da Ofisoshin ’Yan sanda na Shikafi, da kuma ’yan sanda na Musamman da gwamnatin jihar ta dauka kwanan nan.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *