Sace-sace:Kanawa sun koka kan satar allunan makabartu

Tura wannan Sakon

Masu kula da wata maka­barta da ke Gwale a ji­har Kano a Arewacin Nijeriya na ci gaba da kokawa kan irin yadda suka ce ana sa­mun karuwar sace allunan ala­momi na kaburbura.

Masu kula da makabartar sun shaidawa Albishir cewa, tun ku­san watanni uku baya ne suka lura ana yi wa shaidar da ake sakawa kaburbura dauki dai-dai.

Yayin da wadansu kuma al­lunnan suke ganin su a lankwashe idan gari ya waye lamarin da kenuni da cewa, an yi koka­rin cirewa ne amma hakan ta gagara.

Wakilinmu wanda ya je makabartar kafa da kafa, ya ce ya ga kaburbura da dama da aka cire allunan­su aka tafi da su, wadansu kuma a allunan alamarsu a lauye.

Danjuma Labaran na daga cikin masu hakar kabari a wannan makab­arta ta Dandolo, ya kuma bayyanawa Albishir cewa, tun da farko sun fara sa­mun koke ne daga wajen jama’a dangane da batan allunan da suka sanya a kaburburan ‘yan uwansu da aka binne a makabartar.

‘’Muna zargin ‘yan gwan-gwan ne ke zuwa su kwashe su, domin su ne suke yawo a nan wajen, sukan zo su wuce, kuma akwai gefen makabarta da suke irin wadannan ayyu­kan’’ in ji Malam Danju­ma.

Sai dai wadansu masu sana’ar ta tsince-tsincen kayan karafan, watau ‘yan gwangwan a wannan yankin, sun musanta wan­nan zargi da ake yi masu.

Jihar Kano dai na da tarin makabartu da dama da babu hasken wutar lan­tarki, abin da wadansu ke ganin cewa, kan taimaka wajen bayar da mafaka ga masu zuwa su aikata miya­gun laifuffuka a cikinsu.

A wadansu lokuta a baya, an sha samun wad­anda ke shiga makabartu a jihar da tsakar dare domin tone gawarwaki, su ciri wadansu sassan jikinsu da wata mummunar manufa.

Jihar Kano na da mai bai wa gwamna shawara na musamman kan lamu­ran da suka shafi maka­bartu, amma duk da haka wadansu ‘yan jihar na ko­kawa kan yadda ake sa­mun matsaloli irin wad­annan.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *