Shekarau ya caccaki masu son dawo da siyasar dabbanci

Jam iyyar APC da ke Sakkwato ta shawarci tsohon gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau da ya gaggauta karkata akalarsa zuwa Kano in har yana da wata kwarewa ko bajinta a siyasa a maimakon sanya baki a siyasar jihar Sakkwato.

Malam Ibra­him Shekarau

Tura wannan Sakon

Tsohon gwamnan Kano, kuma Sanata mai wakiltar Kano Ta Tsakiya Malam Ibra­him Shekarau, ya bayyana damuwa a kan yadda wasu ‘yan siyasa a jihar ke koka­rin farfado da siyasar daba da aka jima da kawar da ita.

Shekarau ya bayyana hakan ne ya­yin wata hira da Sashen Hausa na BBC, inda ya ce babbar illa ce a ci gaba da yin hamayyar siyasa a Kano kamar yadda ake ganin wasu na yi, ta hanyar daukar maka­mai suna far wa abokan hamayyarsu.

Yana magana ne kan batun fitar da wan­da zai gaji gwamnan jihar mai ci Abdul­lahi Umar Ganduje a zaben 2023, inda ya ce akwai bukatar shugabannin jam’iyyar APC na jihar su yi wa kowa adalci, kada a hana duk mai sha’awa tsayawa takara. Ya ce “Babu laifi masu neman muka­mai su fito, yau in masu neman gwamna sun kai mutum 100 karkashin jam’iyyar APC a Kano duk su fito, abun da kawai muke ganin zai zama illa shi ne ya za­mana ana siyasar gaba, wannan kauyanci ne, shirme ne, kuma ya saba wa tarbiyyar addinin Musulunci ma”, in ji shi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *