Shugabannin kananan hukumomi za su yi rantsuwar kama-aiki -A yau

Tura wannan Sakon

 A yau, gwamnan jihar Kano, Dokta Abdullahi Umar Gan­duje yake jagorantar bikin rantsar da shugabannin kananan huku­momi 43 da aka zaba, a ranar 16 ga Janairu 2021.

Bisa ga dukkan alamu, shugabanni 43 za a rantsar, saboda rasuwar na Be­beji, Alhaji Ali Namadi Bebeji, wanda ya rasu bayan kammala zaben da ‘yan kwanaki.

Jihar Kano, kamar takwarorinta a tarayyar Nijeriya, tana da shiyyoyi uku na majalisar dattijai, Kano ta Are­wa tana da yankunan kananan huku­momi 13, Kudanci na da guda 16, sai Kano ta tsakiya mai guda 15, bi da bi.

Idan aka juya kan sarautun gar­gajiya kuma, akwai masarautu biyar, wadanda suka hada da; Kano, da Bi­chi da Rano, da Gaya da kuma Ka­raye. Biyu daga cikinsu a iya cewa, farfado da su aka yi, watau Rano da Gaya, a yayin da biyu daga cikinsu kirkiro su aka yi, watau Bichi da Ka­raye.

Da yake musayar ra’ayi da edi­tan Triumph, kwamishinan kananan hukumomin jihar, Alhaji Murtala Sule Garo, ya yi alkawarin cewa, ma’aikatarsa za ta bullo da dokar da za ta tilasta wa shugabannin kananan hukumomi, da mukarrabansu zama a yankunansu daban-daban, a maima­kon yin wadari zuwa birnin Kano, babu gaira, babu dalili.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *