Tashin farashi: Kaiwa kololuwa da dalar Amirka ta yi -Atagi

Tashin farashi: Kaiwa kololuwa da dalar Amirka ta yi-Atagi

Alhaji Sagir Yusuf Usman Atagi

Tura wannan Sakon

Daga Wakilinmu

Har yanzu farashin Dala na ci gaba da kawo tsaiko ga har­kokin kasuwanci a jihar Kano dama kasa baki daya, wanda hakan bincike ya nuna shi ya sa farashin kaya a kasuwanni ke kara hauhawa, za ka sayi kaya yau a kasuwa idan ka koma gobe sai ka iske an kara masa farashi.

Bayanin haka ya fito ne daga bakin babban manajan daraktan Atagi General En­terprices da ke kasuwar Kan­tin kwari da ke Kano, Alhaji Sagir Yusuf Usman, a lokacin da yake zanatawa da manema labarai a kan yadda farashin Dalar yake kara hauhawa.

Sakir Yusuf Usman, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da cewa, ta sanya ido sosai ‘yan-kasuwar musayar kud­aden waje watau masu canji saboda ita gwamnati ta ba su a kan Dala 400 da wani abu su kuma suke sayarwa ‘yan-kasuwa fiye da Naira 500.

Har ila yau ita hukumarEFCC ta rika shiga kasuwan­ni domin sanin halin da ake ciki na tsadar Dala, ya bayar da misali kwanakin da suka fara shiga kasuwanni har far­ashin ta ya yi sosai .

Ya ce, matukar gwamnati ba ta takawa abin birki ba, to za’a ci gaba da fuskantar tsa­dar kaya a manya da kananan kasuwanin da ke fadin Nijer­iya, wanda mai karamin karfi shi abin zai fi shafa.

Malam Sagir Yusuf Us­man Atagi , duk da halin da ake ciki yana da kyau yanka­suwa su ci gaba da rangwant­awa masu karamin karfi ka­mar yadda suka yi a lokacin watan Azumin Ramadan da ya gabata, musamman idan sun zo gurinsu kasuwanci.

Daga karshe, ya taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar watan babban Sallah da fatan za’a gudanar da Sallah lafiya ya ba mu al­herin da ke cikinta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *